
ABUBUWA GUDA BIYAR DA YA KAMATA KA SAN SU
$0.02Ka gano muhimman abubuwa guda biyar: zunubi, hukunci, fansa, zarafi da bege na ceto a wurin Yesu Almasihu. Karanta kafin lokaci ya kure.
Quantity
Shipping Cost: $0.00

Ka gano muhimman abubuwa guda biyar: zunubi, hukunci, fansa, zarafi da bege na ceto a wurin Yesu Almasihu. Karanta kafin lokaci ya kure.
Quantity
Shipping Cost: $0.00
“Kamar yadda yake a rubuce cewa,
‘Babu wani mai adalci, babu ko daya ...
gama 'yan adam duka sun yi zunubi,
sun kasa kuma ga daukakar Allah.”
(Romawa 3:10, 23)
“Duk wanda bai tsaya ya aikata duk abin da ke rubuce a littafin shari'a ba,
la’ananne ne.”
(Galatiyawa 3:10)
“Wanda kuwa bai ba da gaskiya ba,
an riga an yi masa hukunci,
don bai gaskata da sunan makadaicin Dan Allah ba.”
(Yahaya 3:18)
“Almasihu ya fanso mu daga la'anan nan ta shari'a
da ya zama abin la’ana saboda mu,
domin a rubuce yake cewa,
**‘Duk wanda aka kafa a jikin itace, la’ananne ne.’”
(Galatiyawa 3:13)
“Almasihu ya mutu domin zunubanmu,
kamar yadda Littattafai suka fada.”
(1 Korantiyawa 15:3)
“Saboda kaunar da Allah ya yi wa duniya
har ya ba da makadaicin Dansa,
domin duk wanda ya gaskata da shi kada ya halaka,
sai dai ya sami rai madawwami.”
(Yahaya 3:16)
“Amma duk iyakar wandanda suka karbe shi,
wato masu gaskatawa da sunansa,
ya ba su ikon zama ’ya’yan Allah.”
(Yahaya 1:12)
“Wanda ya gaskata da Dan,
yana da rai madawwami.Wanda ya ki bin Dan kuwa,
ba zai sami rai ba,
sai dai fushin Allah ya tabbata a gare shi.”
(Yahaya 3:36)
“Ba kuma samun ceto ga wani,
domin ba wani suna duk duniyan nan
da aka bayar cikin mutane,
wanda lalle ta wurinsa ne za mu sami ceto.”
(Ayyukan Manzanni 4:12)
Free tracts and biblical counsel available by request.
Write:
Word Of Truth P.O. Box 1126, Kaduna, Nigeria.
We use cookies to ensure you get the best experience on our website. For more information on how we use cookies, please see out cookie policy. Cookie Policy