Akwai bege...ga mutum kamar ni?
Labari na gaske na tuba da gafara daga zunubi mai nauyi. Akwai bege ga mai laifi! Ka karanta yadda Kristi ke canza rayuwa — ko kai ma.
Labari na gaske na tuba da gafara daga zunubi mai nauyi. Akwai bege ga mai laifi! Ka karanta yadda Kristi ke canza rayuwa — ko kai ma.
Wani dare, bayan taron falkaswa a wani babban guri,
sai wani mutum wanda daga ganin shi yana da hatsari
ya nufi mai wa’azin ya tambaye shi:
“Ko za ka yarda ka zo tare da ni a daren yau?
Domin ina so in yi magana da kai.”
“Da farin ciki kuwa,” mai wa’azin ya amsa.
Sai mutumin ya jagoranci tafiya a titunan anguwan
har zuwa gidan sa.
Sai ya bude kofa,
ya ingiza mai wa’azin zuwa ciki,
daga nan sai ya fitar da bindiga.
“Ba zan yi maka illa ba.
Ina so ne in tambaye ka ko kana nufin abin da ka fada da gaske
ne a wa’azin da kayi da daren nan ne,
cewa jinin Yesu Kristi ya wanke mu daga dukan zunuban mu?”
Mai wa’azin ya amsa mishi cewa:
“Kwarai kuwa, haka nike nufi.
Allah ya fada a cikin maganarsa.”
Sai mutumin ya ce:
“Na kashe mutane hudu da wannan bindigan.
Akwai bege ga mutum kamar ni?”
Mai wa’azin ya ce:
“Na sake gaya maka kuma,
idan mutum zai furta ya kuma rabu da dukan zunuban shi,
Allah ya yi alkawari ya yafe shi,
ya kuma wanke shi daga dukan zunuban shi.”
(1 Yohanna 1:7)
Sai mutumin ya ci gaba da cewa:
“A gefe daya na wannan bangon akwai dandali na.
Muna sayar da barasa ga kowa.
A yawancin lokuta, nikan karbi kudin karshe daga mutum
har ya rasa na sayen abinci ga iyalin sa.A gefen dandalin kuma gidan caca ne da sauran ayyuka na iblis.
Har wani mutum ya taba yin kisan kai domin ya yi asara a wurin.Akwai bege ga mutum kamar ni?”
Mai wa’azin ya amsa da cewa:
“Allah yana nufin idan ya ce,
‘Jinin Yesu Kristi yana wanke mu daga dukan zunuban mu.’”
“Wani tambaya kuma bayan nan sai ka tafi.
Idan ka bar wannan dandalin, za ka wuce gida na.Matana tana tare da diya ta mai shekara goma sha daya.
Shekara goma sha uku da suka wuce,
na sadu da wata yarinya mai kyau a New York,
na yi mata karya akan rayuwa na.Sai ta aure ni, amma bayan da ta tabbatar da gaskiyan,
sai ya raunana mata zuciya.Tun daga wannan lokaci na sa ya zama mata ‘kiyama a duniya.’
Yanzu ma na fara dukan ta.A kwanan nan, na mari diyata har na tura ta,
ta fadi a murhu mai zafi,
wanda ya kone ta daga kafada zuwa ga yatsun ta na hannu.Har hannun ya gurgunce na har abada.
Akwai bege ga mutum kamar ni?”
Mai wa’azin ya kama wannan mutumin,
ya girgiza shi sosai, ya ce:
**“Ka saurare ni da kyau ka ji!
Duk wani irin abin da ka yi a wannan duniya,
maganar Allah tana tsaye:‘Jinin Yesu Kristi yana wanke mu daga dukan zunuban mu.’
Wannan yana nufin kai!”
Sai mutumin yace:
“Na gode sosai.
Na so in tabbata ne.
Na yarda da kai.
Zan sake zuwa wurin taron ku gobe da daddare kuma.”
Bayan da mai wa’azin ya tafi,
sai mutumin ya fitar da dukan kayan cikin mashayarsa
da kayan cacansa.
Ya farfasa kwalabe da gilashi,
ya kakarya teburan caca da kafafunsu,
ya kone ludo da katin caca a cikin wuta.
Dukan tsawon daren,
ya lalatar da dukan kayan da sukan sa shi zunubi.
Har sai da safiya,
sa’annan ya je ya zauna a kofan gidan — a gajiye.
Daga jin shi ya dawo,
sai matan ta ce wa diyar su:
“Ta je ta ce mishi,
Baba, abincin safe yana shirye domin ka.”
Diyar su ta tafi a hankali zuwa ga baban.
Ta bi a tsorace, ta ce mishi:
“Baba, Mama ta ce abincin safe yayi.”
Sai mutumin, da murmushi, ya ce:
“Kaunatacciyar ‘yata,
Baba baya bukatan abincin safe.”
Diyar sa ta koma da gudu zuwa dakin girkin abinci, ta ce:
“Mama! Baba ya yi mini murmushi!
Ya kuma kirani kaunatacce na!
Bai yi mini ihu ba!”
Maman ta ce:
“Ni ban yarda ba!
Koma ki dai fada mishi abincin safe ya nuna.”
Sai maman ta bi ta a baya.
Da mutumin ya ji su suna zuwa, sai ya yi murmushi, ya ce:
“Zo kusa.”
Da rawan jiki,
matan da diyar suka matso kusa da shi.
A hankali ya sa hannayen shi,
ya rungumi su biyu,
da suka sha wuya a hannun shi.
Sai da hawaye a cike a idanun sa,
sai ya tabbatar musu da cewa:
“Kada ku sake jin tsoro na kuma.
Allah ya ba ku sabon Maigida
da sabon Baba a yau.”
A taro na wannan daren,
matan da diyarsu ma suka bada zuciyan su zuwa ga Kristi.
Suma suka tabbatar da cewa:
“Jinin Yesu Kristi yana wanke mu daga dukan zunuban mu.”
(1 Yohanna 1:7)
Ka Sami Sakon? Zaka furta, ka kuma roki gafaran zunuban ka yanzu?
Ka kuma bada ranka zuwa ga Kristi?
Roki Allah ya yafe maka.
Akwai bege domin wani kamar ka!
Free tracts and biblical counsel available by request.
Write: Word Of Truth
P.O. Box 1126, Kaduna, Nigeria
$0.04


Discover why Jesus’ crucifixion was essential for humanity's salvation as confirmed by prophecies and eyewitness accounts!

Explore how God's perfect mercy and justice intersect through the sacrifice of Christ for mankind!

Discover the humble yet noble journey of God's incarnation as Jesus Christ, offering wisdom, love, and forgiveness!

Discover the unique oneness of God and learn how to truly know Him through His infallible word!

Discover your internal enemies and find peace through faith with this inspiring message of salvation!

Discover how Jesus Christ offers a way out of karma with grace and forgiveness, transforming lives today!

Discover if Jesus is the promised Messiah with biblical evidence. Learn how He fulfills ancient prophecies!

Discover the Jewish quest for atonement and how it leads to finding salvation through Jesus' blood. Explore faith beyond rituals!

Explore why the Bible is unshakable and vital through a student's insightful reflection on its enduring impact and divine inspiration. Discover timeless wisdom!

Ponder the crucial timing to think about Christ before it's too late—embrace eternal salvation today!

Discover how God knows your name and guides your life with eternal promise. Embrace faith with a personal touch!

Discover the true meaning of life with Jesus Christ. Find everlasting joy, peace, and fulfillment through faith!

Transform your life through repentance and discover the path to eternal peace with Jesus Christ! 🔄✝️

Discover how to escape the snares of sin and find freedom through Jesus Christ! 🌿✝️

Explore how the Bible offers a path from guilt and sin to forgiveness through Jesus Christ! Transform your story today! 🌟✝️

Discover how faith and belief in Jesus Christ can transform your life. This personal story of an intercollegiate boxing champion reveals the power of salvation! 🌟✝️

Discover life-changing stories of those who gambled with drugs, lost, and found redemption through Jesus Christ. Choose to win! 🌟✝️

Explore the fleeting nature of life and embrace eternal joy through Jesus Christ. Discover how to secure a future beyond earthly bounds.

Discover why living for temporary pleasures can lead to eternal consequences. Find true joy with Christ for a lifetime of happiness. 🌟✝️

Discover the God you didn't know yet! Explore ancient Athens through Paul's eyes and find faith in Jesus today. Embrace a relationship with the true Creator revealed in Scripture. 🌟🙏
We use cookies to ensure you get the best experience on our website. For more information on how we use cookies, please see out cookie policy. Cookie Policy