Akwai bege...ga mutum kamar ni?

Labari na gaske na tuba da gafara daga zunubi mai nauyi. Akwai bege ga mai laifi! Ka karanta yadda Kristi ke canza rayuwa — ko kai ma.

HausaTractsForeign Tracts
Download

Akwai bege...

ga mutum kamar ni?


Wani dare, bayan taron falkaswa a wani babban guri,
sai wani mutum wanda daga ganin shi yana da hatsari
ya nufi mai wa’azin ya tambaye shi:

“Ko za ka yarda ka zo tare da ni a daren yau?
Domin ina so in yi magana da kai.”

“Da farin ciki kuwa,” mai wa’azin ya amsa.

Sai mutumin ya jagoranci tafiya a titunan anguwan
har zuwa gidan sa.
Sai ya bude kofa,
ya ingiza mai wa’azin zuwa ciki,
daga nan sai ya fitar da bindiga.

“Ba zan yi maka illa ba.
Ina so ne in tambaye ka ko kana nufin abin da ka fada da gaske
ne a wa’azin da kayi da daren nan ne,
cewa jinin Yesu Kristi ya wanke mu daga dukan zunuban mu?”

Mai wa’azin ya amsa mishi cewa:

“Kwarai kuwa, haka nike nufi.
Allah ya fada a cikin maganarsa.”

Sai mutumin ya ce:

“Na kashe mutane hudu da wannan bindigan.
Akwai bege ga mutum kamar ni?”

Mai wa’azin ya ce:

“Na sake gaya maka kuma,
idan mutum zai furta ya kuma rabu da dukan zunuban shi,
Allah ya yi alkawari ya yafe shi,
ya kuma wanke shi daga dukan zunuban shi.”
(1 Yohanna 1:7)


Sai mutumin ya ci gaba da cewa:

“A gefe daya na wannan bangon akwai dandali na.
Muna sayar da barasa ga kowa.
A yawancin lokuta, nikan karbi kudin karshe daga mutum
har ya rasa na sayen abinci ga iyalin sa.

A gefen dandalin kuma gidan caca ne da sauran ayyuka na iblis.
Har wani mutum ya taba yin kisan kai domin ya yi asara a wurin.

Akwai bege ga mutum kamar ni?”

Mai wa’azin ya amsa da cewa:

“Allah yana nufin idan ya ce,
‘Jinin Yesu Kristi yana wanke mu daga dukan zunuban mu.’”


“Wani tambaya kuma bayan nan sai ka tafi.
Idan ka bar wannan dandalin, za ka wuce gida na.

Matana tana tare da diya ta mai shekara goma sha daya.
Shekara goma sha uku da suka wuce,
na sadu da wata yarinya mai kyau a New York,
na yi mata karya akan rayuwa na.

Sai ta aure ni, amma bayan da ta tabbatar da gaskiyan,
sai ya raunana mata zuciya.

Tun daga wannan lokaci na sa ya zama mata ‘kiyama a duniya.’
Yanzu ma na fara dukan ta.

A kwanan nan, na mari diyata har na tura ta,
ta fadi a murhu mai zafi,
wanda ya kone ta daga kafada zuwa ga yatsun ta na hannu.

Har hannun ya gurgunce na har abada.
Akwai bege ga mutum kamar ni?”


Mai wa’azin ya kama wannan mutumin,
ya girgiza shi sosai, ya ce:

**“Ka saurare ni da kyau ka ji!
Duk wani irin abin da ka yi a wannan duniya,
maganar Allah tana tsaye:

‘Jinin Yesu Kristi yana wanke mu daga dukan zunuban mu.’

Wannan yana nufin kai!”

Sai mutumin yace:

“Na gode sosai.
Na so in tabbata ne.
Na yarda da kai.
Zan sake zuwa wurin taron ku gobe da daddare kuma.”


Bayan da mai wa’azin ya tafi,
sai mutumin ya fitar da dukan kayan cikin mashayarsa
da kayan cacansa.

Ya farfasa kwalabe da gilashi,
ya kakarya teburan caca da kafafunsu,
ya kone ludo da katin caca a cikin wuta.

Dukan tsawon daren,
ya lalatar da dukan kayan da sukan sa shi zunubi.
Har sai da safiya,
sa’annan ya je ya zauna a kofan gidan — a gajiye.


Daga jin shi ya dawo,
sai matan ta ce wa diyar su:

“Ta je ta ce mishi,
Baba, abincin safe yana shirye domin ka.”

Diyar su ta tafi a hankali zuwa ga baban.
Ta bi a tsorace, ta ce mishi:

“Baba, Mama ta ce abincin safe yayi.”

Sai mutumin, da murmushi, ya ce:

“Kaunatacciyar ‘yata,
Baba baya bukatan abincin safe.”


Diyar sa ta koma da gudu zuwa dakin girkin abinci, ta ce:

“Mama! Baba ya yi mini murmushi!
Ya kuma kirani kaunatacce na!
Bai yi mini ihu ba!”

Maman ta ce:

“Ni ban yarda ba!
Koma ki dai fada mishi abincin safe ya nuna.”

Sai maman ta bi ta a baya.

Da mutumin ya ji su suna zuwa, sai ya yi murmushi, ya ce:

“Zo kusa.”

Da rawan jiki,
matan da diyar suka matso kusa da shi.
A hankali ya sa hannayen shi,
ya rungumi su biyu,
da suka sha wuya a hannun shi.

Sai da hawaye a cike a idanun sa,
sai ya tabbatar musu da cewa:

“Kada ku sake jin tsoro na kuma.
Allah ya ba ku sabon Maigida
da sabon Baba a yau.”


A taro na wannan daren,
matan da diyarsu ma suka bada zuciyan su zuwa ga Kristi.
Suma suka tabbatar da cewa:

“Jinin Yesu Kristi yana wanke mu daga dukan zunuban mu.”
(1 Yohanna 1:7)


Ka Sami Sakon? Zaka furta, ka kuma roki gafaran zunuban ka yanzu?
Ka kuma bada ranka zuwa ga Kristi?
Roki Allah ya yafe maka.
Akwai bege domin wani kamar ka!


Hausa–7 “Is There Hope For A Man Like Me?”

Free tracts and biblical counsel available by request.
Write: Word Of Truth
P.O. Box 1126, Kaduna, Nigeria

Related Products

What is the Truth?

Discover why Jesus’ crucifixion was essential for humanity's salvation as confirmed by prophecies and eyewitness accounts!

Weight of Sin

Explore how God's perfect mercy and justice intersect through the sacrifice of Christ for mankind!

Do you know the humble King?

Discover the humble yet noble journey of God's incarnation as Jesus Christ, offering wisdom, love, and forgiveness!

How to know God

Discover the unique oneness of God and learn how to truly know Him through His infallible word!

Do you know your enemies

Discover your internal enemies and find peace through faith with this inspiring message of salvation!

Karma vs Krupa

Discover how Jesus Christ offers a way out of karma with grace and forgiveness, transforming lives today!

KnowMessiah

Discover if Jesus is the promised Messiah with biblical evidence. Learn how He fulfills ancient prophecies!

Jewish Discovery of a Lifetime

Discover the Jewish quest for atonement and how it leads to finding salvation through Jesus' blood. Explore faith beyond rituals!

Why Believe It?

Explore why the Bible is unshakable and vital through a student's insightful reflection on its enduring impact and divine inspiration. Discover timeless wisdom!

What's Life?

Discover the true meaning of life with Jesus Christ. Find everlasting joy, peace, and fulfillment through faith!

U Turn

Transform your life through repentance and discover the path to eternal peace with Jesus Christ! 🔄✝️

Trapped

Discover how to escape the snares of sin and find freedom through Jesus Christ! 🌿✝️

Those Guilty Stains

Explore how the Bible offers a path from guilt and sin to forgiveness through Jesus Christ! Transform your story today! 🌟✝️

ThisThingWorks

Discover how faith and belief in Jesus Christ can transform your life. This personal story of an intercollegiate boxing champion reveals the power of salvation! 🌟✝️

They Gambled and Lost

Discover life-changing stories of those who gambled with drugs, lost, and found redemption through Jesus Christ. Choose to win! 🌟✝️

Problem with Patty

Explore the fleeting nature of life and embrace eternal joy through Jesus Christ. Discover how to secure a future beyond earthly bounds.

ImHereFor

Discover why living for temporary pleasures can lead to eternal consequences. Find true joy with Christ for a lifetime of happiness. 🌟✝️

GodYouDontKnow

Discover the God you didn't know yet! Explore ancient Athens through Paul's eyes and find faith in Jesus today. Embrace a relationship with the true Creator revealed in Scripture. 🌟🙏

We use cookies

We use cookies to ensure you get the best experience on our website. For more information on how we use cookies, please see out cookie policy. Cookie Policy