Bayan Mutuwa, Ina Zaka Dauwama?
Sakon ceto daga zunubi da hukunci, gayyata zuwa gafara da rai madawwami ta wurin Yesu Kristi. Ka karanta kafin lokaci ya kure.
Sakon ceto daga zunubi da hukunci, gayyata zuwa gafara da rai madawwami ta wurin Yesu Kristi. Ka karanta kafin lokaci ya kure.
Wannan tambaya tana da sukan zuciya.
Mai yiwuwa ne kana ji da lafiya da karfin jiki,
kuma kana gani kamar kana da sauran kwanaki da yawa a duniya.
Idan ba haka ba ne fa?
Idan mutuwa tana kurkusa fiye da yadda kake tunani fa?
Wani mai arziki ya taba fada a ransa ya ce,
“Ina da kaya masu yawa a jibge, tanadin shekara da shekaru.
Bari in huta, in yi ta ci, ni yi ta sha,”
ya da daren nan ana bidar ranka a gare ka” (Luka 12:20).
Mai yiwuwa ne wannan mai arziki gabansa ya fadi da jin cewa
ya rage masu ‘yan awoyi kawai ya bar duniyar.
Ba ka san lokacin da zaka mutu ba.
Kristi yana kwankwasawa a kofar zuciyarka,
yana jira ka bude masa:
Ya ce, “Yau ce ranar ceto” (2 Korintiyawa 6:2).
“Kada ka yi farahiya saboda gobe domin baka san abin da gobe zata kawo ba” (Misalai 27:1).
Ka karbi kyautar ceto da Allah yake baka yanzu —
a yadda kake.
Allah yana lura sosai da dukkan abin da ke tattare da rayuwarka,
kuma “zai tone al’amuran da ke boye a duhu,
ya kuma bayyana nufin zukata” (1 Korintiyawa 4:5).
Ranar da za a tone kowanne boyayyen abu
na tunani da ayyuka a gaban Allah,
akwai ban razana.
Ba ka daukaka shi ba a cikin tunani da ayyuka.
Ba ka gode masa ba yadda ya kamata.
Ka yi ta rayuwa don kanka,
bisa ga taka sha’awa da shiri,
ba tare da ka nemi nufin Allah ba.
Yaya za ka sadu da Allah a cikin wannan rana ta shari’a,
ba tare da mai cetonka ba?
“Sa’annan na ga wani babban kursiyi fari, da wanda ke zaune a kai ...
Sai na ga matattu, manya da yara, tsaitsaye kursiyin,
aka kuma bude littattafai.”
(Ruya ta Yohanna 20:11,12)
Ba za a yi maka shari’a bisa abin da ka yi tunani game da kanka ba,
haka nan kuma ba bisa abin da wasu suke tunaninka ba.
Za a shari’anta maka bisa abin da Allah da kansa ya rubuta cikin wadannan littattafai.
“Aka kwa yi wa matattu shari’a bisa ga abin da ke rubuce cikin littattafan,
gwargwadon aikin da suka yi.”
(Ruya ta Yohanna 20:12)
Allah yana ganin duk wani tunani da wata manufa da ke cikin zuciyar mutum.
Ya san kowanne tunani na asiri da kuma duk wani abin da aka aikata a boye.
“Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce a Littafin Rai ba,
sai a jefa shi a tafkin nan na wuta.”
(Ruya ta Yohanna 20:15)
Babu wanda zai tsere wa shari’a,
sai ko wadanda aka sami sunayensu a cikin Littafin Rai.
Ka yi tunani wani dan lokaci kadan akan
abin da Yesu Kristi ya yi domin ka a bisa giciye.
“Domin Almasihu ma ya mutu sau daya tak ba kari,
domin kawar da zunubanmu, mai adalci saboda marasa adalci,
domin ya kai mu ga Allah.”
(1 Bitrus 3:18)
“Shi kansa ya dauke zunubanmu a jikinsa a kan gungume.”
(1 Bitrus 2:24)
“Ubangiji ya sa hukunci ya auko a kansa.
Hukuncin da ya wajaba a kanmu.”
(Ishaya 53:6)
“Shi Almasihu ma, da aka mika shi hadaya sau daya tak,
domin ya dauke zunuban mutane da yawa.”
(Ibraniyawa 9:28)
“Jinin Yesu Dansa kuma yana tsarkake mu daga dukkan zunubi.”
(1 Yohanna 1:7)
“Ta haka kauna take, wato ba mu bane muka kaunaci Allah ba,
sai dai shi ne ya kaunace mu, ya aiko Dansa, hadayar sulhu saboda a gafarta zunubanmu.” (1 Yohanna 4:10)
Ka yi tunanin abin da Yesu Kristi ya bayar.
Ya hakura da daukakarsa, domin ya sha wahala a bisa giciye,
domin mu kubuta daga shari’a kuma mu zauna a sama tare da shi har abada.
“Ba kaunar da ta fi haka ga mutane, wato mutum ya ba da ransa saboda aminansa.”
(Yohanna 15:13)
“Yadda muka san kauna ke nan , wato ta wurin ba da ransa da ya yi saboda mu.”
(1 Yohanna 3:16)
A shirye yake ya karbe ka
ya kuma gafarta maka dukkan zunubanka
idan har ka furta su.
Ka zo gare shi da kowanne irin hali kake da shi, ko kuma kake ciki.
Ka saurara ka ji ga shi yana kiranka, yana cewa:
“Ku zo gare ni, dukanku da ku ke wahala,
masu nauyin kaya kuma, ni kuwa zan baku hutawa.”
(Matta 11:28)
Ka zo yanzu.
Idan ka bari sai gobe, ai yiwuwa ne ka makara.
Hausa–4 “Where Will You Spend Eternity?”
Free tracts and biblical counsel available by request. Write:
Word Of Truth
P.O. Box 1126, Kaduna, Nigeria.
$0.04


Discover why Jesus’ crucifixion was essential for humanity's salvation as confirmed by prophecies and eyewitness accounts!

Explore how God's perfect mercy and justice intersect through the sacrifice of Christ for mankind!

Discover the humble yet noble journey of God's incarnation as Jesus Christ, offering wisdom, love, and forgiveness!

Discover the unique oneness of God and learn how to truly know Him through His infallible word!

Discover your internal enemies and find peace through faith with this inspiring message of salvation!

Discover how Jesus Christ offers a way out of karma with grace and forgiveness, transforming lives today!

Discover if Jesus is the promised Messiah with biblical evidence. Learn how He fulfills ancient prophecies!

Discover the Jewish quest for atonement and how it leads to finding salvation through Jesus' blood. Explore faith beyond rituals!

Explore why the Bible is unshakable and vital through a student's insightful reflection on its enduring impact and divine inspiration. Discover timeless wisdom!

Ponder the crucial timing to think about Christ before it's too late—embrace eternal salvation today!

Discover how God knows your name and guides your life with eternal promise. Embrace faith with a personal touch!

Discover the true meaning of life with Jesus Christ. Find everlasting joy, peace, and fulfillment through faith!

Transform your life through repentance and discover the path to eternal peace with Jesus Christ! 🔄✝️

Discover how to escape the snares of sin and find freedom through Jesus Christ! 🌿✝️

Explore how the Bible offers a path from guilt and sin to forgiveness through Jesus Christ! Transform your story today! 🌟✝️

Discover how faith and belief in Jesus Christ can transform your life. This personal story of an intercollegiate boxing champion reveals the power of salvation! 🌟✝️

Discover life-changing stories of those who gambled with drugs, lost, and found redemption through Jesus Christ. Choose to win! 🌟✝️

Explore the fleeting nature of life and embrace eternal joy through Jesus Christ. Discover how to secure a future beyond earthly bounds.

Discover why living for temporary pleasures can lead to eternal consequences. Find true joy with Christ for a lifetime of happiness. 🌟✝️

Discover the God you didn't know yet! Explore ancient Athens through Paul's eyes and find faith in Jesus today. Embrace a relationship with the true Creator revealed in Scripture. 🌟🙏
We use cookies to ensure you get the best experience on our website. For more information on how we use cookies, please see out cookie policy. Cookie Policy